in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rikicin Boko Haram na korar 'yan Najiriya zuwa Chadi, in ji hukumar HCR
2014-06-21 16:25:32 cri
Hare-haren kungiyar Boko Haram da ayyukan sojojin Najeriya a cikin kasar na tilastawa mutane fice wa zuwa yankunan kasar Chadi masu wuyar shiga na tafkin Chadi a tsawon shekaru biyu na baya bayan nan, in ji Mamadou Diam Balde wakilin mataimakin hukumar 'yan gudun hijira ta HCR a ranar Jumma'a. Musanyar wuta tsakanin mayakan Boko Haram da rundunar sojojin tarayyar Najeriya ta tilastawa daruruwan mutane gudun garuruwan Madai, Falatimi, Amalewa, Bagakawa, Kalakime, Dougori da wasu kauyukan dake kuriyar arewacin Najeriya, in ji wannan jami'in.

Wata tawagar hadin gwiwa a karkashin jagorancin gwamnatin Najeiya, HCR, PAM da wasu kungiyoyin bada agaji masu zaman kansu da ta isa garuruwa biyu dake yankin tafkin Chadi a farkon watan Mayu ta gano 'yan Najeriya dake gudun hajira 1077 daga cikin iyalai 285 da suka gudu daga Najeriya dalilin tashe tashen hankali da na ayyukan keta hakkin dan Adam. Haka kuma tawagar ta kididdige 'yan asalin Chadi 361 daga cikin iyalai 55 da suka baro Najeriya. Hukumar HCR da abokan huldarta sun taimakwa 'yan gudun hijirar Najeriya da na Chadi da kayayyakin bukatun yau da kullum. Haka kuma da wasu sauran 'yan gudun hijira da wadanda aka kwashe da ma 'yan asalin sauran kasashe kamar Mali, na iyar kasancewa cikin wannan yankin, ko da yake zuwa wannan wuri na da matukar wuya, in ji mista Dian Balde.

A cewar jami'in na HCR, yawancin mutanen da suka isa Chadi daga su sai tufafi kuma suna cin abinci sau daya a jini. Suna bukatar abinci, ruwan sha, mazugunni, tsafta da kiwon lafiya. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China