in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNIDO za ta tallafawa Najeriya wajen bunkasa masana'antu
2014-06-22 15:51:30 cri

Hukumar bunkasa ci gaban masana'antu ta MDD UNIDO, ta bayyana aniyar tallafawa tarayyar Najeriya wajen aiwatar da tsare-tsare, da za su kai ga cimma nasarar manufofin kasar a fannin bunkasar masana'antu.

Hakan a cewar ministan ma'aikatar lura da masana'antu, cinikayya da zuba jari a kasar Olusegun Aganga, ya biyo bayan kyakkyawan shirin da mahukuntan kasar ke yi a wannan fanni. Inda ya ce hakan ne ma ya sanya gwamnatin kasar mai ci, kaddamar da sabon shirin gaggauta bunkasar masana'antu na NIRP.

Mr. Aganga ya kara da cewa shirin NIRP da za a kwashe shekaru 5 ana gudanarwa, zai share fagen bunkasar kananan masana'antu, da samar da guraben ayyukan yi.

Kaza lika shirin zai bada karfi ga habaka sassan da kasar ke da karfi ta fuskar masana'antu, ciki hadda fannin masana'antu dake sarrafa albarkatun gona, da sashen ma'adanai, da na albarkatun mai da iskar gas da dai sauransu.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China