in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara zaben shugaban kasa a Masar
2014-05-26 19:58:54 cri
A yau ne Misirawa suka fara kada kuri'a a zaben shugaban kasa a karon farko tun bayan da aka hambarar da tsohon shugaban kasar Mohamed Morsi.

Tsohon babban hafsan sojojin kasar Abdel Fattah al-Sisi wanda ya jagoranci tumbuke gwamnatin Morsi da jagoran masu ra'ayin mazan jiya Hamdeen Sabahy ne kawai za su fafata a zaben.

Al-Sisi ya kara samun farin jini tun lokacin da ya hambarar da Morsi a watan Yulin da ya gabata,bayan boren gama garin da aka yiwa gwamnatinsa ta shekara guda,abin da ake ganin zai taimaka masa cikin sauki wajen samun galaba a kan Sabahy, mutumin da ya zo na uku a zaben shugaban kasar na shekarar 2012. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China