in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya taya Abdul Fattah al-Sisi murnar lashe babban zaben shugaban Masar
2014-06-05 20:21:51 cri
A jiya ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya buga waya ga Abdul Fattah el-Sisi inda ya taya shi murnar lashe babban zaben shugaban kasar Masar da aka yi.

Shugaba Xi Jinping ya ce, kasar Masar ita ce kasa ta farko cikin kasashen Afirka da Larabawa da suka kulla dangantakar diflomasiyya da kasar Sin, kuma dangantakar kasashen biyu na ci gaba da bunkasa cikin yanayi mai kyau cikin shekaru 58 da suka gabata ne aka kulla dangantakar diflomasiyya a tsakanin kasar Sin da kasar Masar. Kuma kasar Sin za ta ci gaba da bunkasa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu bisa manyan tsare-tsare kuma cikin dogon lokaci, tana fatan ci gaba da yin hadin gwiwa tare da kasar Masar wajen zurfafa dadadden zumuncin dake tsakanin jama'ar kasashen biyu, karfafa hadin gwiwa kan fannoni daban daban, ciyar da hadin gwiwar kasashen biyu bisa manyan tsare-tsare gaba, don tallafawa kasashen biyu da kuma al'ummominsu (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China