in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar MDD ta sanar da babbar matsalar rashin samun kudin tallafi na gudanar da ayyuka a yankin Sahel da kuma na Kuryar Afrika
2012-05-11 15:47:44 cri
Hukumar kula da abinci da ayyukan gona ta MDD wato FAO ta yi gargadi a ranar Alhamis cewa, rashin samun kudin tallafi domin gudanar da ayyuka a yankin Sahel da na Kuryar Afrika wata babbar matsala ce, kamar yadda kakakin hukumar Martin Nesirky ya sanar.

"yau hukumar FAO ta yi wannan kira, duk da cewa, ana samun daidaito kan yadda za a samar da abinci mai inganci da kuma hanyoyin ci gaba, amma samar da kudi ya kasance wata babbar matsala", cewar Nesirky a gaban manema labarai. Ya kara da cewa, misali mai bada tsoro shi ne FAO ta rasa samun kudi wajen gudanr da ayyukanta a yankin Sahel da yankin Kuryar Afrika.

Kamar yadda Nesirky ya ce, babban jami'in hukumar FAO ya damu matuka game da rashin damar taimakawa mutanen da ke cikin bukata a yankin Kuryar Afrika.

Nesirky ya kuma nuna cewa, a lokacin da yake jawabi a yayin taron tattalin arziki na kasa da kasa a birnin Madrid na kasar Spain, Jose Graziano da Silva, babban direktan hukumar FAO ya furta cewa, a yankin Kuryar Afrika, hukumar tana rashin damar kara samun nasarorin da za su taimaka wajen kawar da bala'in karancin abinci da ya faru a shekarar bara a kasar Somalia, lamarin ya kara karya kwarin gwiwar iyalai da dama da ke fuskantar bala'in fari. (Abdou Halilou)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China