in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban jami'in hukumar FAO ya yaba wa kokarin da kasar Sin ta yi wajen kawar da talauci
2013-06-04 16:46:05 cri
A ranar 3 ga wata, babban jami'in hukumar kula da abinci da aikin gona ta M.D.D. Jose Graziano da Silva ya rubuta wani bayani mai taken "Fasahar da Sin ta samu wajen cimma nasarar yaki da talauci a duniya" a shafin Internet na Xinhua da ke kasar Sin, inda ya bayyana cewa, kokarin da kasar Sin ta yi shi ne, babban dalilin kawar da talauci da yunwa a duniya.

Silva ya bayyana cewa, a cikin shekaru 20 da suka gabata, yawan mutanen da suke fama da matsalar yunwa ya ragu da miliyan 100 a kasar Sin. A cikin shirin raya kasa na M.D.D. da aka tsara a shekara ta 2000, an ce, an yi shirin rage rabin yawan mutanen da suke fama da talauci da yunwa zuwa shekarar 2015, kuma kasar Sin na kokarin cimma wannan buri. To, Amma, wannan ya danganta ne ga gyare-gyaren da gwamnatin Sin ke yi game da aikin gona da kauyuka da kuma saka musu jari.

A cikin bayanin, Mr. Silva ya ce, don kafa wata duniya da ta samu dauwamammen ci gaba da babu mayunwata, kamata ya yi kasashen duniya su cusa sabbin abubuwa wajen habbaka tattalin arziki, game da wannan, kuma kasar Sin tana da fasahohi masu amfani.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China