in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar FAO za ta gwada wani sabon shiri a wasu kasashe hudu
2013-03-14 10:36:32 cri
Ran 13 ga wata, ta shafin intanet din ta, hukumar MDD mai kula da harkokin hatsi da ayyukan noma ta FAO, ta sanar da cewa, za ta gwada wani sabon shirinta a wasu kasashe hudu, shirin da zai taimaka wajen binciken halin karancin abinci na kasa da kasa cikin sauri.

Bisa labarin da aka samu, an ce, sunan wannan sabon shiri shi ne 'muryar masu fama da karancin abinci'. Bugu da kari a halin yanzu, hukumar ta FAO ta riga ta tsai da kudurin, na gwada wannan sabon shiri a kasashen Angola, da Habasha, da Malawi da kuma Nijar. Yayin da ake gudanar da aikin 'muryar masu fama da karancin abinci', za a zabi wakilan jama'a dubu daya zuwa biyar daga kowace kasa cikin kasashen 4, domin su amsa tambayoyi takwas, da haka, za a tantance ko cikin watanni sha biyu da suka gabata, wadannan jama'a da kungiyar ta zaba sun taba gamu da matsalar karancin abinci, ko a'a, tare kuma da fayyace yanayin fama da matsalar da suke ciki. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China