in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'an kasashen Afirka masu kula da harkar watsa labaru sun ziyarci CRI
2014-06-17 16:37:24 cri
A Talatar nan ne wasu jami'an kasashen Afirka fiye da 50, wadanda suke halartar taron huldar hadin gwiwar Sin da Afirka kan harkokin watsa labarai, suka kawo ziyara nan gidan rediyon kasar Sin CRI.

A jawabinsa na maraba da bakin, mataimakin shugaban gidan radiyon na CRI mista Xia Jixuan, ya ce CRI na samun ci gaba wajen yada labarai da shirye-shiryensa ga al'ummun nahiyar Afirka.

Mr. Xia, ya kara da cewa CRI na fatan karin hadin gwiwa tare da kafofin watsa labaru na kasashen Afirka, musamman ma a fannonin musayar shirye-shirye da ma'aikata, da fassarar fina-finai, da raya kafofin watsa labarai na zamani da dai sauransu. Duka da nufin karfafa huldar hadin gwiwa dake tsakanin Sin da Afirka a fannin watsa labarai, da kuma burin kara dankon zumunci tsakanin bangarorin 2. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China