in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kakakin ma'aikatar harkokin waje ta Sin ya amsa tambayar 'yan jarida kan maganar jami'in majalisar gudanarwa ta Amurka dangane da tekun Kudu na Sin
2014-02-09 17:30:37 cri
Jiya Asabar 8 ga wata, yayin da yake amsa tambayar 'yan jarida kan maganar jami'in majalisar gudanarwa ta Amurka dangane da tekun Kudu na Sin, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta Sin Hong Lei ya bayyana cewa, Sin tana da ikon mallakar tekun Kudu bisa tarihi, kuma ikonta na samun kariya daga dokokin kasa da kasa.

Wani dan jarida ya tambaya cewa, ranar 5 ga wata, a gun taron sauraron kara, mataimakin sakataren harkokin waje na Amurka, Daniel Russel ya bayyana cewa, Sin ta gwada iko da moriyarta a yankin teku bisa layin iyakar kasar a tekun Kudu, wannan bai dace da dokokin kasa da kasa ba. Kamata ya yi a yi bayani kan wannan batu ko a kyautata matsayin kasar Sin. Game da wannan batu, mene ne ra'ayin kasar Sin?

Dangane da wannan, Hong Lei ya amsa cewa, game da rikici kan yankin teku tsakanin Sin da wasu sauran kasashe, Sin ta dade tana kokarin daidaita wannan batu ta hanyar yin shawarwari tsakaninta da kasashen da abin ya shafa kai tsaye. A sa'i daya, Sin tana dora muhimmanci kan tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a wannan yankin teku ta hanyar tabbatar da 'sanarwar ayyukan kasashen dake yankin teku na Kudu' tare da kasashe membobin kungiyar ASEAN. Sin ta bayyana matsayinta a fili. Ta da zaune tsaye ba zai taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a kudu maso gabashin Asiya ba. Maganar wasu jami'an Amurka a gun taron sauraron kara ba ta da ma'ana ko kadan.

Dadin dadawa, Hong ya kara da cewa, ana kalubalantar Amurka da ta bayyana ra'ayinta cikin adalci, domin taka rawar a zo a gani wajen tabbatar da zaman lafiya da bunkasuwa a wannan yanki.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China