in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a gaggauta kawo karshen matakan soji a gabashin kasar Ukraine cewar Poroshenko
2014-06-09 10:43:33 cri
Sabon shugaban kasar Ukraine Petro Poroshenko, ya shaidawa manema labaru cewa za a kawo karshen matakan soja da ake dauka a yankin gabashin kasar ta Ukraine kafin nan da karshen wannan mako.

Shugaba Poroshenko wanda ya bayyana hakan a jiya Lahadi, ya yi wani taron tattaunawa tsakaninsa da bangarori uku da batun siyasar yankin gabashin kasar ya shafa don lalubo hanyar aiwatar da shirin wanzar da zaman lafiya a yankin.

Har wa yau shugaba Poroshenko ya jaddada cewa, abu mafi muhimmanci a hanlin yanzu shi ne, mayar da tsarin gudanarwa a yankin gabashin kasar ta Ukraine, tare da tabbatar da tsaron rayukan jama'ar kasar dake zaune a yankin.

A dai ranar ta Lahadi an yi wani babban gangami a filin 'yancin kai dake birnin Kiev, inda wakilan jama'a suka bayar da wata sanarwa, wanda suka bukaci majalisar dokokin kasar ta yanzu, da sabon shugaban kasar Poroshenko, su tabbatar da lokacin gudanar da zaben majalisar dokokin kasar ba tare da bata lokaci ba. Ban da wannan, sanarwar ta kuma bukaci majalisar dokokin kasar da ta aiwatar da tsarin raba kujerunta bisa yawan kuri'un da jam'iyyun kasar suka samu, da kuma fatan majalisar za ta rage yawan kuri'un da jam'iyyu ke samun iznin shiga majalisar da su, daga kashi 5 zuwa kashi 3 cikin dari, domin idan har aka ci gaba da bin ka'idar yanzu, kungiyar siyasa da mahalarta babban taron jama'ar da suka hallara a filin 'yancin kai, ba ta da damar shiga majalisar dokokin kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China