in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya ja hankalin gwamnatin Masar da ta dauki matakan wanzar da zaman lafiya
2014-06-04 11:07:47 cri
Babban magatakardar MDD Ban Ki-moon, ya ja hankalin gwamnatin kasar Masar, da ta kara himma wajen tabbatar da yanayin zaman lafiya da lumana mai dorewa a kasar.

Cikin wata sanarwa da kakakinsa ya fitar a jiya Talata, biyowa bayan bayyana sakamakon zaben kasar ta Masar, Mr. Ban ya ce ya maida hankali kwarai ga wannan sakamako na zaben da ya gudana daga 26 zuwa 28 ga watan Mayun da ya shude. Ya kuma yi imani da cewa, sabon shugaban kasar ta Masar zai yi kokari wajen biyan bukatun jama'ar kasar, musamman ma a fannin wanzar da zaman lafiya da wadata, da bunkasa dimokuradiyya a kasar.

Haka zalika sanarwar ta ce, Ban Ki-moon ya jaddada aniyar MDD ta ci gaba da bada gudummawa da goyon baya ga kasar Masar kamar yadda ta saba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China