in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta nuna damuwarta kan rashin ci gaba da aka samu daga shawarwarin da ake yi a Mali
2014-04-24 12:01:14 cri
A ran 23 ga wata, kwamitin sulhu na MDD ya fitar da wata sanarwa, inda ya nuna damuwa kan rashin ci gaba da aka samu daga shawarwari tsakanin gwamnatin Mali da dakaru masu makamai. Kwamitin yayi kira ga bangarorin da abin ya shafa da su daddale yarjejeniyoyi cikin sauri domin kawo karshen rikicin kasar.

Sanarwar ta ce, kwamitin sulhu ya yi kira ga gwamnatin Mali, da bangarori daban daban wadanda suka cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta Ouagadougou, da dakaru masu makamai dake arewacin Mali wadanda suka yanke dangantaka da kungiyoyin ta'addacni da yarda da shiga cikin yarjejeniyar ba tare da sharadi, da su cimma matsaya daya ba tare da bata wani lokaci ba kan wata taswirar shawarwari dake budewa ga sassa daban daban dake arewacin kasar, da kuma samu amincewa daga wajensu, domin daidaita matsalar kasar ta hanyar siyasa, ta yadda za a iya girmamawa zaman karko na dogon lokaci, da 'yancin kasa, da dinkuwar kasa, da cikakken yankin kasa.

Sanarwar ta ce, kwamitin sulhu ya yi maraba da matakin da shugaban kasar Mali Ibrahim Boubacar Keita ya dauka na nada wani jami'in da zai wakiltarsa a cikin shawarwari na gaba.

A wannan rana, kwamitin sulhu na MDD ya shirya wani taro kan halin da ake ciki a kasar Mali, inda ministan harkokin wajen Mali ya yi kira ga MDD da kasashen duniya da su kara ba da taimako ga tawagar tabbatar da zaman karko ta MDD dake Mali, ta yadda za ta iya gudanar da ayyukanta yadda ya kamata. (Danladi)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China