in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta yi kokarin shiga aikin tabbatar da tsaro da zaman lafiya da bunkasuwar Asiya
2014-05-30 20:22:57 cri
A Yau Jumma'a 30 ga wata ne, kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin Qin Gang ya bayyana a nan birnin Beijing cewa, Sin za ta yi kokarin shiga shawarwarin tabbatar da tsaro da zaman lafiya da bunkasuwar Asiya.

A daren yau ne kuma, za a bude taron Shangri-La a Singapore. Game da wannan batu, Qin ya bayyana a gun taron manema labaru cewa, wannan muhimmin dandali ne na yin shawarwari kan harkokin tsaron Asiya, shi ya sa Sin take dora muhimmanci sosai a kai.

An labarta cewa, mataimakin babban hafsan hafsoshin rundunar sojan 'yantar da jama'ar kasar Sin, Wang Guanzhong zai jagoranci tawagar Sin domin halartar taron, yayin da darektar kwamitin harkokin waje na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin, madam Fu Ying ita ma za ta halarci taron bisa goron gayyata.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China