in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a gudanar da bikin baje koli na tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da kasashen Afirka karo na farko a kasar Sin
2014-05-27 11:04:19 cri
An shirya gudanar da bikin baje kolin game da tattauna batutuwan tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da kasashen Afirka karo na farko a birnin Qingdao dake kasar Sin tun daga ranar 26 zuwa ta 29 ga watan nan na Yuli.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, burin bikin shi ne fara hadin gwiwa a fannoni uku, wato hadin gwiwa a tsakanin kamfanoni da hukumomin gwamnatocin kasashen Afirka, da tsakanin kamfanoni da masu sayen kaya na kasashen waje, da kuma tsakanin kamfanonin kasar Sin da kamfanonin kasashen Afirka. A gun bikin, za a yi kokarin kara yin hadin gwiwa a tsakanin Sin da kasashen Afirka a fannonin albarkatun ma'adinai, gina ababen more rayuwa, da kera na'urori, sadarwa, aikin gona, yawon shakatawa da dai saurausu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China