in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin babban hafsan hafsoshin rudunar sojan kasar Sin zai halarci taron Shangri-La
2014-05-29 20:16:57 cri
A Yau Alhamis 29 ga wata, kakakin ma'aikatar tsaron kasar Sin Geng Yansheng ya shelanta cewa, daga ranar 30 ga watan Mayu zuwa 2 ga watan Yunin bana, mataimakin babban babban Janarhafsan hafsoshin din rundunar sojan 'yantar da jama'ar kasar Sin, Wang Guanzhong zai jagoranci tawagar Sin domin halartar taron shawarwari na Shangri-La da za a yi a Singapore.

Geng ya sanar da hakan ne a taron manema labaru na ma'aikatar tsaron kasar da aka yi a yau, inda ya bayyana cewa, a yayin wannan taro, Wang zai yi jawabi, domin bayyana ra'ayin tsaron Asiya da shugaba Xi na kasar Sin ya gabatar a taron koli na inganta cudanya da karfafa hadin gwiwa ta nahiyar Asiya, da gabatar da ayyukan da rundunonin sojan Sin suka yi domin tabbatar da wannan ra'ayi na tsaron Asiya da yin hadin gwiwa da sauran kasashen duniya a fannin tsaro, kuma Wang ya zai yi kira dagabatar da kirayinsa na a karfafa hadin gwiwa a fannin tsaro tsakanin shiyya-shiyya.

Ban da haka, an labarta cewa, a yayin taron, Wang zai gana da shugabannin hukumomin tsaron kasa da Janar din rundunonin soja na wasu sauran kasashen duniya da abin ya shafa, domin yin musayar ra'ayi kan yanayin tsaro na shiyya-shiyya da dangantakar a tsakanin rundunonin sojansu.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China