in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamata ya yi kamfanonin kasashen waje da ke Sin su dace da moriya da tsaron kasar Sin
2014-05-28 20:42:05 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin, Qin Gang ya bayyana a nan birnin Beijing cewa a yau Laraba cewa, ko da yake Sin tana gudanar da manufar bude kofarta ga kasashen waje, amma dole ne kamfanonin kasashen waje dake kasar su girmama dokokin Sin, kuma su dace da moriya da tsaron kasar yadda ya kamata.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, yanzu gwamnatin Sin tana yin nazari kan tsaron na'urar IBM da ake amfani da ita.

Game da wannan batu, a gun taron manema labaru da aka shirya a wannan rana, Qin Gang ya furta cewa, a zamanin yau, tsaron yanar gizo ta intanet da tsaron sakwanni na da muhimmanci kwarai da gaske ga tsaron kasa. Shi ya sa gwamnatin Sin za ta gabatar da ka'idojin da abin ya shafa nan ba da dadewa ba, a kokarin kara tabbatar da tsaro a wadannan fannoni. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China