in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a kaddamar da tattaunawa a duk fadin kasar Ukraine bayan da Petro Poroshenko ya zama shugaban kasar
2014-05-27 15:09:16 cri
A ranar 25 ga wata, an kammala babban zabe a kasar Ukraine, kuma bisa sakamakon binciken ra'ayin jama'a da aka yi wa masu zabe, Petro Poroshenko zai zama sabon shugaban kasar. A ranar 26 ga wata kuma, Mr. Poroshenko ya bayyana cewa, idan ya zama shugaban kasar, zai kai ziyara a yankin Donbas domin tattaunawa tare da mazauna wurin. Haka zalika, yana fatan zuwa kasar Rasha domin tattaunawa da shugabannin kasar.

Bugu da kari kuma Mr. Poroshenko ya jaddada cewa, Rasha, babbar kasar dake makwabtaka da kasar Ukraine. Kuma dole sai da taimakon kasar Rasha, wajen kawo karshen yaki da samun zaman lafiya a Ukraine, da ma samun kwanciyar hankali a wannan shiyya.

A waje daya kuma, yankunan da ke kudu maso gabashin kasar Ukraine na ci gaba da cikin halin rudani. A ranar 26 ga wata, sojojin gwamnatin kasar Ukraine sun tafka karamin fada da dakaru a filin jiragen sama na birnin Donetsk, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutum a kalla daya. Kuma bisa labarin da kamfanin dillancin labaru na Rasha ya bayar, an ce, sojojin kasar Ukraine su yi amfani da jiragen sama masu saukar ungulu 6 zuwa 8, da kuma jiragen saman yaki 2 wajen luguden boma bomai, a yayin dakarun 'yan a ware suka rika amfani da makaman roka domin maida martani. (Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China