in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar dokokin kasar Ukraine ta zartas da takardar bayani kan hakuri da juna da zaman lafiya
2014-05-21 10:22:39 cri

A ranar Talata 20 ga wata, majalisar dokokin kasar Ukraine ta zartas da "Takardar bayani kan hakuri da juna da zaman lafiya" ta hanyar kada kuri'a.

A cikin takardar, an bayyana cewa, majalisar ta goyi bayan "Takardar Geneva" da Ukraine da Amurka da kungiyar EU da kuma Rasha suka cimma matsaya a kai a ranar 17 ga watan jiya, haka kuma ta nuna goyon baya da a tattauna a duk fadin kasar bisa tsarin taron sulhuntar al'umma, da shirya babban zabe a ranar 25 ga wata.

Bugu da kari kuma majalisar ta yi Allah wadai da yin amfani da makamai ba bisa doka ba da kuma ta da hargitsin nuna kin jinin juna.(Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China