in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude taron shugabannin mambobin kungiyar kasashe 'yan ba-ruwanmu karo na 16
2012-08-30 20:32:19 cri
A ranar Alhamis 30 ga wata, a birnin Tehran, babban birnin kasar Iran ne aka bude taron shugabannin mambobin kungiyar kasashe 'yan ba-ruwanmu karo na 16, wanda za a dauki kwanaki 2 ana yinsa, inda za a tattauna da rattaba hannu kan daftarin sanarwar karshe da aka zartas a yayin taron ministocin harkokin wajen kasashe mambobin kungiyar.

A bikin bude taron, shugaba Mohamed Morsi na kasar Masar ya mika ikon shugabancin kungiyar a hannun Iran. Ya bayyana fatansa cewa, Iran za ta shugabanci kungiyar yadda ya kamata, tare da inganta rawar da kungiyar ke takawa a duk duniya. Ya kara da cewa, tun can da kuma zuwa yanzu kungiyar na taka muhimmiyar rawa wajen wanzar da adalci a duniya da goyon bayan kasashe masu tasowa. Mohamed Morsi ya yi kira ga kungiyar da ta kyautata kanta, ci gaba da mara wa kasashe masu tasowa baya, kara azama kan wanzar da adalci da zaman lafiya a duniya, a kokarin taka rawa mai kyau a tsarin kasa da kasa.

A jawabinsa a bikin, Ali Khamenei, shugaban addini na Iran ya ce, kasarsa ba za ta yi watsi da ikon yin amfani da makamashin nukiliya cikin lumana ba. Sa'an nan kuma Ban Ki-moon, babban magatakardan MDD ya kalubalanci Iran da ta dauki matakai domin kau da damuwar kasashen duniya kan shirinta na nukiliya.(Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China