in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An rufe taron shugabannin kasashen kungiyar 'yan ba ruwanmu karon 16
2012-09-01 17:17:20 cri

An rufe taron shugabannin kasashen kungiyar 'yan ba ruwan mu karon 16, wanda aka kwashe kwanaki 2 ana yinsa, a daren ranar 31 ga watan Augusta, a birnin Tehran, fadar mulkin kasar Iran. A wajen taron an zartas da wasu takardun da suka bayyana yadda za a raya harkokin kungiyar 'yan ba ruwanmu a shekaru 3 masu zuwa.

Shugaban taron wannan karo, kuma shugaban kasar Iran, Mahmoud Ahmadinejad, ya ce takardun da aka zartas sun hada da 'sanarwar Tehran', dake kunshe da batun cigaba da nuna goyon baya ga Palesdinu, da dai makamantansu. Ban da haka, an tsai da kudurin kira taron shugabannin kungiyar karon 17 a kasar Venezuela a shekarar 2015.

A cewar shugaba Ahmadinejad, mahalarta taron sun yarda da dukufa kan kokarin cimma burin kungiyar 'yan ba ruwanmu, kana sun yi kira da a yi kwaskwarima kan tsarin da ake bi wajen kula da harkokin duniya, ta yadda za a sanya dukkan kasashen duniya su shiga wannan aiki, don tabbatar da zaman lafiya a duniya. Har ila yau, mahalarta taron sun amince da kare hakkin bil Adama, da tabbatar da mutuncin mutum, gami da kokarin magance tashin hankali. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China