in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi mamakin hukuncin kisa da aka yanke a Masar
2014-03-26 10:56:35 cri
Mataimakin kakakin babban sakataren MDD, Mista Farhan Haq ya bayyana a jiya 25 ga wata cewa, babban ofishin kwamishina mai kula da harkokin bil Adama na majalissar, ya yi matukar mamaki, kan hukuncin kisa da aka yankewa sama da mutane 500 a kasar Masar, a ranar 24 ga watan nan, matakin da ofishin ke ganin ya yi matukar sabawa dokokin kare hakkin bil Adama na duniya.

Game da ra'ayin babban sakataren MDD kan hakan, Farhan Haq ya ce, Ban Ki-Moon ya goyi bayan ra'ayin wannan ofishi, zai kuma ci gaba da mayar da hankali kan batun.

Ban da wannan kuma, ofishin ya bayyana cewa, abin da aka fi damuwa da shi shi ne, kame mutane sama da dubu bisa ta'addanci da ake musu tun cikin watan Yulin bara.

A ranar 24 ga watan nan ne dai kotun lardin Minya dake kudancin kasar ta Masar, ta yanke wa mambobin kungiyar 'yan uwa Musulmi, da masu goyon bayan kungiyar 528 hukuncin kisa, sakamakon zargin su da kaiwa ofishin 'yan sanda farmaki, matakin da ya haddasa mutuwar 'dan sanda guda, a wata zanga-zanga da aka yi a watan Agustan bara. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China