in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Pakistan zai halarci bikin rantsar da takwaransa na Indiya
2014-05-24 21:18:55 cri
Kamfanin dillancin labaru na Pakistan ya ba da labari a yau Asabar 24 ga wata cewa, bisa goron gayyatar da bangaren kasar Indiya ya yi masa ne, Nawaz Sharif, firayin ministan kasar Pakistan zai halarci bikin rantsar da takwaransa na Indiya. Wannan shi ne karo na farko da wani babban jami'in Pakistan zai halarci bikin kama aikin firaminsitan kasar Indiya, tun bayan da kasashen biyu suka samu 'yancin kai a shekarar 1947. Wannan wani sabon ci gaba ne ta fuskar dangantaka tsakanin kasashe biyu, idan aka dubi zaman doya da man ja da suke yi cikin shekaru da dama.

Narendra Modi zai yi rantsuwar kama aiki a ranar 26 ga wata, tun bayan da aka bada sakamakon babban zabe a kasar Indiya. Kafin wannan, jam'iyyar Bhartiya Janta ta Indiya (BJP) ta mista Modi ta bayyana cewa, Indiya ta riga ta gayyaci shugabannin kasashe membobin kungiyar hadin gwiwa ta shiyya-shiyya ta kudancin Asiya(SAARC)domin halartar bikin kama aikin mista Modi, ciki har da kasar Pakistan.

Indiya da Pakistan sun taba yin yaki sau uku tsakaninsu cikin shekaru sama da 10 da suka gabata, kuma a kan samu rikici tsakanin kasashen biyu game da yankin Kashmir, lamarin dake kara tsananta yanayin dangantakar kasashen biyu. A shekarar bara, firaministan Pakistan Nawaz Sharif ya taba gayyatar tsohon firaministan Indiya Manmohan Singh domin ya halarci bikin kama aikinsa, amma ba tare da samun nasarar zuwan takwaransa na Indiya ba.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China