in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Sin Li Keqiang ya fara kai ziyara a kasar Indiya
2013-05-19 20:18:15 cri
Bisa gayyatar da firaministan kasar Indiya ya yi masa, firaministan kasar Sin Li Keqiang ya isa birnin New Delhi a yammacin lahadi 19 ga wata a farkon ziyararsa ta kwanaki 3 a kasar Indiya.

Karamin ministan harkokin waje na kasar Indiya da sauran manyan jami'an kasar ne suka tarbe shi a filin jiragen sama. A jawabinsa bayan saukarsa Mr Li Keqiang ya lura cewa, a matsayin manyan kasashe masu tasowa biyu a duniya, Sin da Indiya suna kiyaye dangantakarsu yadda ya kamata, wanda ya dace da moriyar kasashen biyu, kana zai taimakawa wajen kiyaye zaman lafiya da wadata a nahiyar Asiya har ma a fadin duniya baki daya. Ya ce a don haka, gwamnatin kasar Sin ta dora muhimmanci sosai kan raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Indiya, kana ta maida kasar Indiya a matsayin muhimmiyar abokiya a duniya. Li Keqiang ya yi imani da cewa, ziyararsa a wannan karo za ta sa kaimi ga kara yin mu'amala, hadin gwiwa, fahimtar juna da kuma sada zumunta a tsakanin kasashen biyu, kuma hakan zai taimaka wajen inganta dangantakar abokantaka ta hadin gwiwa da kiyaye zaman lafiya da wadata a tsakaninsu a nan gaba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China