in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin ya jaddada cewa, moriyar Sin da Indiya ta bai daya ta fi sabanin da ke tsakaninsu
2013-05-10 20:06:03 cri
Ranar 10 ga wata, Li Keqiang, firaministan kasar Sin ya gana da ministan harkokin wajen kasar Indiya Salman Khurshid.

A yayin ganawar, Li Keqiang ya ce, moriyar kasashen Sin da Indiya ta bai daya ta fi sabanin da ke tsakaninsu. Kasar Sin tana son yin kokari tare da Indiya wajen warware batun iyakar kasashensu ta hanyar yin shawarwari kuma cikin lumana, a kokarin samar da kyakkyawan yanayi wajen yin hadin gwiwa a tsakaninsu.

Har wa yau Li Keqiang ya ce, sabuwar gwamnatin kasar Sin tana mai da hankali kan raya dangantaka a tsakaninta da Indiya, tana son inganta amincewa da juna ta fuskar siyasa a tsakaninta da Indiya, zurfafa hadin gwiwar da ke tsakaninsu, da kara yin tuntubar juna a kan al'amuran kasa da kasa, a kokarin kiyaye da raya dangantakar yin hadin gwiwa da abokantaka a tsakanin kasashen 2 bisa manyan tsare-tsare.

A nasa bangaren kuma, Salman Khurshid ya ce, kasar Indiya tana son hada kai da kasar Sin wajen nuna wa kasashen duniya tabbacin- cewa, kasashen 2 na amincewa da juna da mara wa juna baya, sa'an nan za su tinkari sabanin da ke tsakaninsu yadda ya kamata, a kokarin warware batun iyakar kasashensu yadda ya kamata.(Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China