in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta ci gaba da sa kaimi ga gudanar shawarwarin nukiliya na kasar Iran
2014-05-19 20:22:09 cri
Hong Lei, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin, ya bayyana a nan birnin Beijing, ranar 19 ga wata, da cewa, kasar Sin za ta ci gaba da kokarin sa kaimi ga gudanar shawarwari dangane da batun nukiliya na kasar Iran.

Manyan kasashe 6 da batun nukiliya na kasar Iran ya shafa, da kungiyar kasashen Turai EU, da kasar Iran, sun yi shawarwari a zagaye na 4 a birnin Viena na kasar Austria don tsara wani kundin yarjejeniya da zai shafi dukkan fannonin wannan batun.

Game da lamarin, mista Hong Lei ya ce, hakan na nufin shawarwarin ya fara tabo wasu abubuwa masu muhimmanci da sarkakiya, don haka za a iya gamuwa da wasu matsaloli, amma dukkan bangarorin da batun ya shafa sun nuna niyyar neman cimma matsaya daya nan da nan. Don haka kasar Sin na fatan ganin an ci gaba da tattaunawa cikin daidaituwa, da kulawa da bukatun kowane bangare, ta yadda za a iya cimma wata yarjejeniyar da ta shafi fannoni daban daban a niyyar da ka nuna. A nata bangaren, kasar Sin za ta ci gaba da kokarin sa kaimi ga wannan aiki, in ji kakakin kasar Sin. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China