in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta bukaci bangarorin dake gaba da juna a Sudan ta Kudu dasu sassauta
2014-05-16 20:46:47 cri
Kasar Sin ta bukaci bangarorin dake gaba da juna a Sudan ta Kudu dasu kara sassauta zaman zullumi dake tsakanin su sannan kuma su cika alkawarin da suka dauka na tabbatar da zaman lafiya da tsaro a nahiyar Afrika.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin Madan Hua Chunying wadda ta bayyana hakan a ranar jumma'an nan lokacin taron manema labarai tace kasar na fatan ganin yunkurin daga dukkan bangarorin da hakan ya shafa wanda zai taimaka wajen ragen zaman zullumi a kasar Sudan ta Kudu.

Bangarorin masu gaba da juna a Sudan ta Kudu dukkan su sun rattaba hannu akan wata yarjejeniya a ranar 9 ga watan nan da muke ciki wanda a ciki aka amince zasu dakatar da bude wuta sannan a kafa gwamnatin rikon kwarya domin shirin babban zabe a cikin shekara daya. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China