in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin da ke adawa da gwamnatin Sudan ta Kudu sun dauki niyyar kifar da gwamnatin kasar
2014-04-16 11:00:04 cri

Shugaban sojojin da ke adawa da gwamnatin kasar Sudan ta Kudu, kuma tsohon mataimakin shugaban kasar Riek Machar ya sanar a ran 14 ga wata cewa, za su kai hari birni Juba na kasar da kuma wasu muhimman filayen hakar mai, da zumma tunbuke shugaba mai ci Salva Kiir daga kujerarsa.

A lokacin da yake hira tare da manema labaru a wani kebabben wurin da ke jihar Nile, ya bayyana cewa, Kiir na mulkin kama karya, kuma ba shi da hujjar more ikon mukamin kasar. Idan ba za a kore shi daga mukaminsa ba, ba za'a kawo karshen yakin basasa ba.

Mista Machar ya ci gaba da cewa, yana fatan bangarorin biyu za su girmama yarjejeniyar tsagaita bude wuta da suka daddale a watan Janairu na bana. Kuma yana fatan zai iya yin shawarwari tare da Kiir, fuska da fuska, amma wannan kusan ba zai iyu ba. (Danladi)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China