Iyaye,Malaman makarantar dalibai da 'yan uwansu sun gane fuskokin wadanda aka nuna a faifan bidiyon lokacin da aka nuna shi a gidan gwamnati dake birnin Maiduguri,kamar yadda kakakin gwamnatin jihar Isa Gusau ya sanar.
A cikin wata sanarwar da ya sanya ma hannu Malam Isa Gusau ya yi bayanin cewa a cikin wadanda aka sabcen aka kuma nuna wassu a wannan faifan bidiyon,an tantance fuskokin 77 daga cikin su ta zayyana sunayen su da Iyaye, Malamai da masu gadin makarantar har ma da wassu daga cikin daliban da suka tsere bayan an sace su suka yi lokacin da suke kallon bidiyon. (Fatimah Jibril)