in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Olusegun Obasanjo ya la'anci sace daliban Chibok da aka yi
2014-05-13 18:41:34 cri

sohon shugaban kasar Najeriya, Olusegun Obasanjo ya yi Allah wadai da sace daliban Chibok da aka yi a jihar Borno. Obasanjo ya bayyana hakan ne a wani taro da ya halarta a birnin Dutse da ke jihar Jigawa a jiya.

Obasanjo ya kuma yi kira ga wadanda suka sace daliban da su yi gaggawar sako 'yan matan domin ba su yi musu laifin komai ba, don haka kada su wahalar da su ba tare da hakkin komai ba.

"Kowane irin fushi wadannan mutane suke ji da shi, bai kamata a ce sun huce a kan yaran da ba su ji ba su gani ba." In ji Obasanjon.

"Don haka mun yi Allah wadai da abin da suka aikata, kuma muna kira gare su da su sako yaran, saboda suna da gudummuwa mai muhimmaci da za su iya bayarwa ga kasar a nan gaba", in ji tsohon shugaban kasar.

Har wa yau kuma, Obasanjo ya taya iyayen yaran jaje, amma kuma ya kara da cewa kada hakan ya sa wasu iyaye sun ki sanya 'ya'yansu mata makaranta. Ya kuma yi fatan za'a gano yaran, har a mika su ga iyayensu nan bada jimawa ba.(Murtala)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China