in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Faransa na shirin tattauna wa tare da kasashen Amurka da Birtaniya kan batun yaki da kungiyar Boko Haram
2014-05-13 15:18:36 cri

Bisa labarin da kafofin watsa labarai na kasar Faransa suka bayar, an ce, shugaban kasar Francois Hollande ya bayyana a ranar 12 ga wata a Yerevan babban birnin kasar Armenia cewar, kasarsa ta riga ta gayyaci kasashen Amurka da Birtaniya wajen halartar taron da za ta shirya a birnin Paris bisa kokarin yaki da kungiyar Boko Haram mai tsattauran ra'ayin kishin Islama ta kasar Najeriya, wadda ta yi garkuwa da dalibai 'yan mata fiye da 200.

Shugaba Hollande ya kara da cewa, za a kira taron ne domin maida hankali kan wannan matsala, a maimakon jita jitar dake nuna cewa kasar Faransa za ta dauki matakin soja a kasar Najeriya. Haka kuma a yayin wannan taro za'a yi kokarin bullo da matakan yaki da kungiyar Boko Haram, kuma kasar Faransa za ta bada nata taimako.

Ya jaddada cewa, dole ne a yaki da kungiyar Boko Haram a maimakon neman sulhu tare da ita.(Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China