in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta ware sama da rabin tallafin kasarsa ga kasashen Afirka ba tare da sharadi ba
2014-05-08 20:08:04 cri

Firaministan kasar Sin Li Keqiang, ya ce kasar sa za ta baiwa nahiyar Afirka sama da rabin kason da take warewa domin tallafawa kasashen ketare.

Mr. Li wanda ya yi wannan alkawari gaban mahalarta taron tattalin arziki na duniya da ake gudanarwa kan Afirka a Abuja, babban birnin tarayyar Najeriya. Ya kara da cewa kamar ko da yaushe, Sin za ta dada agajin da take baiwa nahiyar Afirka, ba kuma tare da gindaya wani sharadi ba.

Kazalika Mr. Li ya ce kasar Sin a shirye take ta taimakawa kasashen Afirka wajen samar da ababen more rayuwa, da suka kunshi layukan dogo, da manyan hanyoyin mota, da habaka harkar sufurin jiragen sama. Ya ce za a baiwa sashen hadin gwiwa tsakanin sassan biyu, musamman a fannin samar da ababen more rayuwa cikakkiyar kulawar da ta dace. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China