in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yaba ma jawabin da Firaministan Sin ya yi a cibiyar AU
2014-05-07 17:27:06 cri
A ran Talata 6 ga wata,ministan kula da harkoki tsara birane da gidaje na kasar Nijer Habi Mahamadou Salissou ya yaba ma jawabin da firaministan kasar Sin Li Keqiang ya yi a cibiyar kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU, ya na mai cewa, tsarin hadin gwiwar dake tsakanin kasar Sin da Afirka da firaminista Li ya bayyana na da muhimmiyar ma'ana wajen ciyar da hadin gwiwar dake tsakanin bangarorin biyu gaba.

Malam Salissou wanda ya halarci babban taron zuba jari kan kayayyakin more rayuwa na Macao karo na biyu da aka yi nan birnin Beijing, a lokacin zantawarsa da wakilin Gidan Rediyon CRI na musamman, ya bayyana cewa, a halin yanzu, kasar Sin na dukufa wajen cimma burinta, don haka kasar Nijer ita kuma tana kokarin wajen cimma nata burin na shirin raya tattalin arziki tsakanin shekarar 2012 da ta 2015, da kuma shirin samar da isassun abinci da kanta.

A cewar ministan yana fatan tsarin hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka da firaministan Li Keqiang ya bayyana zai iya taimakawa kasashen biyu wajen cimma burinsu tare. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China