Gwamantin kasar Nijar ta cimma wasu sabbin matakan da suka shafi aiwatar da dokar dake nasaba da hakar ma'adinan kasar, a cewar wani sakamakon zaman taron ministocin kasar da ya gudana a ranar Jumma'a, lasin yin bincike da kuma lasin hakar ma'adinai sun kasance na dogaro da yarjejeniyar ma'adinai da gwamnati za ta sanya hannu nan gaba tare da wanda ko wadanda suka samu wadannan lasisi daga lokacin da suka same su.
A cewar sabbin matakan da wannan sabon kudurin da gwamnatin Nijar ta sanya ma hannu sun nuna cewa yarjejeniyoyin da aka sanya ma hannu a baya za su ci gaba da aiki har sai lokacin karshen wa'adinsu. Sabon kudurin na yanzu ya kawo gyaran fuska da kuma kari bisa ga na tsohon kudurin da aka dauka a shekarar 2006. (Maman Ada)