in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Faransa ta yaba wa kokarin da Nijar take yi wajen tabbatar da zaman lafiya a shiyyar Sahel
2014-02-05 16:05:44 cri
Ministan harkokin wajen kasar Faransa, Laurent Fabius, ya nuna yabo a ranar Talata kan muhimmin kokarin da kasar Nijar take yi wajen tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a yankin Sahel, a yayin wata ganawarsa a birnin Paris tare da takwaransa na kasar Nijar, Mohamed Bazoum.

Ganawar tsakanin wadannan manyan jami'ai biyu ta taimaka wajen yin tilawar muhimman batutuwan dake ciwa yankunan na Afrika tuwo a kwarya, musamman ma matsalolin tsaro da ake fuskanta a kasashen Sahel da kasar Libiya.

Ya tabbatar da kusancin ra'ayoyinmu da kuma amincewa da juna dake tasiri a cikin dangantakarmu, in ji kakakin fadar Quai d'Orsay.

Musamman ma, mista Fabius ya nuna babban yabo kan kokarin da kasar Nijar take yi wajen tabbatar da zaman lafiya a yankin Sahel, in ji kakakin. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China