in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar AU ta yi maraba da cigaban da aka samu na samar da zaman lafiya a Sudan ta kudu
2014-03-06 20:43:47 cri
Shugaban kwamitin Kungiyar Tarayyar kasashen Afrika AU Madam Nkosazana Dlamini-Zuma tayi maraba da cigaban da aka samu a kokarin samar da zaman lafiya a kasar Sudan ta kudu,bayan makwanni biyu da aka yi ana ta tattaunawa akan cimma matsaya da tsarin da za'a bi a siyasance domin samar da sulhu da kuma waraka abin da ake fuskanta.

Madam Nkosazana Zuma ta yaba matuka ga wakilan musamman na kungiyar raya gwamnatocin gabashin Afrika IGAD wadanda sune suka yi ta shiga tsakani wajen tattaunawa tsakanin bangarorin biyu na kasar Sudan ta kudun, a cewar ta kokarin wadannan masu shiga tsakanin ne ya sa aka samu dawo da tattaunawa aka kuma kai inda ake a yanzu.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China