in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani jami'in MDD ya bukaci gamayyar kasa da kasa da ta kara rubanya kokarinta a Afrika ta Tsakiya
2014-05-02 15:59:40 cri
Da yake bayanin cewa gamayyar kasa da kasa bata cika alkawuranta ba a kasar Afrika ta Tsakiya dake fama da kazamin yakin basasa da babbar asarar rayukan jama'a, shugaban dake kula da ayyukan jin kai na MDD yayi kira a ranar Alhamis ga kara tura jami'an tsaro da kuma kara samar da kudade domin taimaka wa wajen kawo karshen wannan rikici.

John Ging, darektan ayyukan cibiyar daidaita harkokin agaji ta MDD (OCHA), ya shaida wa manema labara cewa dakarun sa kai na kristoci dana musulmai za su kara zafafa wutar gaba tsakanin kabilun kasar, kana kuma mutanen sun yi watsi da imaninsu wajen kara zafafa wutar kiyayya da tashe tashen hankali da ba'a taba ganin irinsu ba.

Mista Ging, da ya dawo daga garin Boda dake kudancin kasar Afrika ta Tsakiya, ya bayyana cewa ya kuma kara nuna damuwarsa kan wani sabon abun tashin hankali, wato al'ummar Afrika ta Tsakiya na zargin yanzu kristoci da musulmai, maimakon nuna yatsa ga gungun kungiyoyin dake dauke da makamai kamar yadda suke a da. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China