in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Birnin Baku ya mika bukatar daukar bakuncin wasannin gasar ci kofin kasashen turai ta 2020
2014-05-01 17:18:04 cri
Rahotanni daga ofishin hukumar kwallon kafa ta Turai UEFA, na cewa birnin Baku na Azerbaijan, ya mika bukatar daukar bakuncin wasannin zagayen karshe, na gasar cin kofin kasashen turai da za a yi a shekarar 2020.

Bisa kuma tsari, hukumar ta UEFA za ta nazarci, tare da tantance bukatar da birane masu fatan daukar bakuncin wasannin suka gabatar, kafin daga bisani ta mika rahotonta ga babban kwamitin zartaswar ta. Kaza lika ana sa ran bayyana birane 13 da za a amince su karbi bakuncin gasar a ranar 19 ga watan Satumbar shekarar nan, a birnin Geneva na kasar Switzeland.

A yayin wani taron kwamitin zartaswar hukumar ta UEFA na shekarar 2013 ne dai aka yanke shawarar baiwa birane 13 da za a zaba, damar daukar bakuncin zagayen karshe, na gasar cin kofin kasashen na Turai na shekarar ta 2020.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China