in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Uganda ta tura sojojin MDD fiye da 1,600 a kasar Somaliya
2014-02-05 16:34:25 cri
Rundunar sojojin kasar Uganda ta turo a kwanakin baya wani sabon rukunin sojojin kiyaye zaman lafiya na MDD fiye da 1,600 zuwa kasar Somaliya domin taimakawa ayyukan tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin wannan kasa, in ji rundunar sojojin kasar a ranar Talata a birnin Kampala.

Sojojin tawagar yaki ta kasar Uganda (UGABAG) za'a jibge su a shiyya ta daya a kasar ta Somaliya dake karkashin kulawar sojojin kasashen Uganda da Burundi, in ji kakakin sojojin Uganda Paddy Ankunda a cikin wata hirarsa ta wayar tarho tare da kamfanin dillancin labarai na Xinhua.

Wadannan sojojin za'a jibge su ta yadda ya dace a wannan shiyya ta daya, kuma za su taimaka wajen karfafa zaman lafiya da tsaro a yankunan da aka barbe daga hannun mayakan kungiyar Al-shebab, in ji mista Ankunda.

Sojojin na Uganda da Burundi, a karkashin tawagar kungiyar tarayyar Afrika dake kasar Somaliya (AMISOM), an jibge su a wannan shiyya ta daya dake kunshe da yankunan Banadir, Bas da Moyen-Shabelle da kuma shiyya ta uku da ta hada yankunan Baie da Bakool. Haka kuma sojojin suna gudanar da aikin sintiri a Mogadiscio, babban birnin kasar da kuma garin Markal. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China