in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban kasar Sin ya gana da ministan harkokin wajen Tanzaniya
2014-02-25 20:29:53 cri

Yau Talata 25 ga wata, a nan Beijing, Li Yuanchao, mataimakin shugaban kasar Sin ya gana da Bernard Kamillius Membe, ministan harkokin wajen kasar Tanzaniya.

A yayin ganawar, mista Li ya ce, Sin da Tanzaniya sun kulla dankon zumunci a tsakaninsu, kuma su aminai ne a ko da yaushe. Kasar Sin na fatan aiwatar da ra'ayi daya da shugabannin kasashen 2 suka cimma daga dukkan fannoni ta hanyar amfani da damar cikon shekaru 50 da kulla huldar diplomasiyya a tsakaninsu, tare da zurfafa kyakkyawar hadin gwiwarsu a fannoni daban daban, a kokarin raya huldar abokantaka da hadin gwiwa a tsakaninsu daga dukkan fannoni domin samun moriyar juna da nasara tare da kuma kawo wa jama'arsu alheri.

A nasa bangaren kuma, mista Membe ya ce, kasarsa ta darajta dadadden zumunci da ke tsakaninta da Sin, don haka tana son himmantuwa wajen kara habaka hadin gwiwar da ke tsakaninsu a fannoni daban daban.(Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China