in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zimbabwe ta yi bikin samun 'yancin kanta shekaru 34 da suka wuce
2014-04-19 17:14:30 cri
Ranar Jumma'a 18 ga wata ta kasance zagayowar ranar cika shekaru 34 da kasar Zimbabwe ta samu 'yancin kanta. Domin murnar wannan rana, jama'ar kasar fiye da dubu 50 sun halarci wani bikin da aka gudanar a wani babban filin wasan dake birnin Harare, fadar mulkin kasar, inda shugaban kasar Robert Mugabe ya nuna cewa tattalin arzikin kasar na fuskantar kalobaloli, ban da haka kuma ya yi Allah wadai da kungiyar kasashen Turai EU kan matakan da ta dauka na nuna kin jinin gwamnatin kasar Zimbabwe.

Yayin da tattalin arzikin kasar Zimbabwe ke samun farfadowa a shekarun baya, yana ci gaba da fuskantar wasu matsaloli, musamman ma rashin isashen kudi a kasuwa bayan da ta yi watsi da kudin kanta sa'an nan ta fara amfani da dalar Amurka. A cikin jawabinsa, shugaba Mugabe ya jaddada cewa, gwamnatinsa na kokarin daukar matakai don daidaita wannan matsala, ta yadda za a kau da shingen da ya hana a ci gaba da raya masana'antun kasar.

Ban da haka kuma, dangane da takunkumin da kasashen yammacin duniya suke ci gaba da saka ma kasar Zimbabwe, shugaba Mugabe ya soki kungiyar kasashen Turai, inda ya ce kungiyar na son ci gaba da kin amincewa da gwamnatin dake karkashin jagorancin Zanu-PF. Duk da cewa an yi babban zabe bisa doka, amma kungiyar EU ta ce wai an aikata magudi a wajen zaben.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China