in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNICEF yayi kira da a dauki matakan magance karancin abinci ga yara a Sudan ta Kudu
2014-04-13 15:54:35 cri
Wakilin ofishin asusun yara na UNICEF a kasar Sudan ta Kudu Jonathan Veitch, ya yi kira da a kara zage damtse wajen daukar matakan magance karancin abinci dake addabar yara kanana a kasar.

Veitch ya ce kasar Sudan ta kudu na sahun gaba a jerin kasashen da yara ke fuskantar karanci abinci mai gina jiki, inda kimanin yara 250,000 ke fuskantar barazanar hakan, nan da karshen wannan shekara da muke ciki.

Wakilin asusun na UNICEF ya alakanta wannan barazana da yaran kasar ke ciki, da rashin damar gudanar da aikin noma yadda ya kamata, sakamakon tashe-tashen hankulan dake addabar kasar. Ya ce tuni wani kaso mai yawa, na yaran kasar suka fada wannan layi na kamfar abinci mai gina jiki, cikin shekaru 2 da rabi da kasar ta shafe bayan samun 'yancin kai a shekarar 2011.

Har wa yau Veitch ya jaddada muhimmanci daukar matakan gaggawa, domin kaucewa rasa rayukan yara kimanin 500,000, wadanda ya ce na iya rasuwa muddin ba a hanzarta kaiwa kasar dauki ba.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China