in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi zargin keta hakkin bil'adama a Sudan ta Kudu
2014-02-22 16:05:59 cri
Wani kwarya kwaryar rahoto, da ofishin tawagar wanzar da zaman lafiyar MDD a Sudan ta Kudu ya fitar, ya yi zargin keta hakkokin bil'adama a wasu jihohin kasar, sakamakon dauki ba dadin da tsagin dakarun gwamnati, da na 'yan adawar kasar ke yi.

Wata sanarwa da ta fito daga ofishin na UNMISS ta ce, rahoton wanda tuni aka mika shi ga kwamitin sulhun MDD, ya kunshi bayanai kan zargin kisan fararen hula, da amfani da karfin tuwo, tare da keta alfarmar wasu al'ummu bisa dalilai na kabilanci.

A cewar rahoton, tsakanin 15 ga watan Disambar bara zuwa watan Janairun nan da muke ciki, al'ummun jahohin Jonglei, da tsakiyar Equatoriya, da Unity da kuma jihar Upper Nile, na cikin wadanda wannan balahira ta fi shafa.

Bugu da kari, ofishin na UNMISS ya ce zai fidda wani cikakken rahoto, don gane da halin da ake ciki a kasar ta Sudan ta kudu, musamman kan batun keta hakkin bil Adama, a cikin watan Afirilu mai zuwa. (Saminu Alhassan Usman)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China