in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi maraba da kafuwar rundunar wanzar da zaman lafiya ta MINUSCA
2014-04-11 11:00:55 cri
Babban sakataren MDD Ban ki-Moon, ya yi maraba da tabbatar kudurin kwamitin tsaron majalissar na tura dakarun wanzar da zaman lafiya a kasar Afirka ta tsakiya karkashin tawagar MINUSCA.

Mr. Ban wanda ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da kakakinsa ya fitar, ya ce zartas da wannan kuduri muhimmin mataki ne, da zai kawo karshen tashe-tashen hankula dake aukuwa tsakanin dakarun sa kai na musulmi da na mabiya addinin kirista, rikicin dake neman kaiwa ga kisan kiyashi a kasar.

Sanarwar ta kuma ruwaito Ban na yabawa kokarin da rundunonin MISCA, da ta kasashen Turai dake aikin kare zaman lafiya a Afirka ta tsakiyar, yana mai cewa MDD za ta ci gaba da hada kai da su wajen karfafa ayyukan sabuwar rundunar MINUSCA.

Karkashin wannan kuduri na kafuwar rundunar MINUSCA dai kwamitin na tsaro zai samar da dakarun tsaro 10,000, wadanda suka hada da masu sanya ido 240, da masu aikin soji 200, da kuma 'yan sanda 1,800.

Har wa yau, kwamitin tsaron ya yanke shawarar mika ikon rundunar wanzar da zaman lafiya ta kasashen Afirka MISCA zuwa ga sabuwar rundunar ta MINUSCA a ranar 15 ga watan Satumba mai zuwa. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China