in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan kunar bakin wake 4 sun mutu a Maiduguri
2014-04-02 16:25:45 cri

Wasu 'yan kunar bakin wake su Hudu da ake kyautata zaton 'yan ta'adda ne, sun rasa rayukansu yayin da suke kokarin kai hari ofishin hukumar NNPC dake birnin Maiduguri na jihar Borno.

Daraktan yada labarun rundunar tsaron kasar, Chris Olukolade ne ya bayyana hakan, yana mai cewa lamarin ya auku ne a wani karamin gari, mai suna Mulai dake daf da birnin na Maiduguri.

Manjo-Janar Olukolade ya ce motoci uku daga cikin hudu, da suke dauke da bama-bamai sun yi fata-fata, sakamakon budewa wuta da sojojin suka yi kan maharan, lamarin da ya sanya bama-baman dake cikin motocin tarwatsewa.

Sojoji biyar sun samu raunuka, sai dai har zuwa yanzu ba'a tabbatar da adadin fararen hular da harin ya shafa ba, a cewar Olukolade.

Bisa labarin da muka samu, an ce, bama-baman sun fashe ne da misalin karfe biyu na ranar talata, a garin na Mulai, dake kusa da gidan rediyon Peace FM, wanda harin ya taba wani bangare na ginin harabar sa.

Garin Mulai na da nisan kilomita 5 ne kacal da cikin garin Maiduguri, kuma gari ne da daruruwan mutane suke hada-hada da kai-kawo a kullum, tun bayan da aka kafa wani babban gidan man fetur, mallakin gwamnatin tarayya a cikin sa.(Murtala)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China