in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Najeriya sun fara daukar muhimman matakan tsaro a jihohin Benue, Nassarawa da Filato
2014-04-01 20:25:41 cri

Rundunar sojin tarayyar Najeriya a ranar Litinin din nan ta bayyana cewa ta fara daukar muhimman matakan tsaro na soja a jihohin Benue, Nassarawa da kuma Filato, da zummar kawo karshen tashe-tashen hankali, da murkushe gungun mutane masu tada kayar-baya.

A cikin wata sanarwar da aka fitar a Abuja, babban birnin Kasar ,babban jami'in sashin watsa labarai na rundunar tsaron kasar manjo-janar Chris Olukolade ya bayyana cewa, matakan sojan da ake dauka zasu kawo karshen yawan kashe-kashen da ake yi, da kuma hasarar rayuka da dukiyoyi da aka samu a wadannan wurare.

Mista Olukolade ya ce an riga an jibge sojojin sama, da 'yan sanda da kuma jami'an tsaro da dama a Benue, Nassarawa da Filato, a wani kokari na farfado da zaman lafiya da kwanciyar hankali a wuraren da suke zaune cikin fargaba saboda rashin zaman lafiya.

Janar Olukolade ya kuma yi kira ga mazauna wadannan jihohin uku da su bada hadin-kai ga sojojin gwamnatin, ta kokari samar da bayanai masu amfani domin taimakawa aiwatar da matakan tsaro yadda ya kamata.(Murtala)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China