in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya gana da Jean Marc Ayrault, firaministan kasar Faransa
2014-03-27 21:20:21 cri
A yau Alhamis 27 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping wanda ke ziyara a kasar Faransa ya gana da Jean Marc Ayrault, firaministan kasar Faransa, inda Mr. Xi ya nuna cewa, kasashen Sin da Faransa sun fitar da shirin bunkasa dangantakar dake tsakaninsu irin na matsakaita da dogon lokaci, wannan zai taimakawa wajen bunkasa harkokin cinikayya a tsakaninsu da zuba jari ga juna. Ya kuma yi fatan bangaren Faransa zai samar da yanayin zuba jari mafi kyau ga kamfanonin kasar Sin, har ma kasashen biyu za su iya kara yin hadin gwiwa da sauran kasashe tare.

A nasa bangaren, Mr. Ayrault ya bayyana cewa, bangaren Faransa yana hangen nesa game da huldar dake tsakaninsa da kasar Sin daga dukkan fannoni, kuma yana son ci gaba da yin tattaunawa kan harkokin siyasa da sauran batutuwa iri daban daban. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China