in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Amurka sun dauki niyyar hada kai wajen yaki da ta'addanci da manyan laifuffukan kasa da kasa
2014-03-25 11:59:59 cri

Shugabannin kasashen Sin da Amurka sun bayyana ra'ayoyinsu a ranar Litinin a birnin Hague domin karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen nasu biyu wajen yaki da ta'addanci da manyan laifuffukan kasa da kasa.

A yayin wata ganawa da takwaransa na kasar Amurka Barack Obama a yayin taron tsaron nukiliya a birnin Hague, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana cewa, yana yabawa sosai da matsayin da Obama ke dauka wajen yin allahwadai da duk wani nau'in ta'addanci, kuma kasar Sin a shirye take wajen yin aiki tare da dukkan kasashe, har ma da Amurka domin yaki da ta'addanci.

Mista Xi ya kuma yi kira da a karfafa hadin gwiwa tsakanin 'yan sandan kasar Sin da na Amurka a cikin fannonin da suka hada da yaki da manyan laifuffukan kasa da kasa, da kuma farautar da mutanen da suke gujewa gurfana gaban kuliya.

A nasa bangare, mista Obama ya jaddada matsayinsa na yin allahwadi da harin ta'addancin da ya faru a birnin Kunming dake kudu maso yammacin kasar Sin, tare da bayyana cewa, kasarsa na adawa da duk wani nau'in ta'addanci, kuma yana allahwadai da duk wasu ayyukan ta'addanci a duk inda suka faru.

Kasar Amurka a shirye take ta karfafa hadin gwiwa wajen yaki da ta'addanci tare da kasar Sin, in ji Barack Obama. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China