Kakakin ma'aikatan harkokin wajen ta kasar Sin Hong Lei ya sanar da hakan a yau Litinin a taron manema labarai da aka saba yi duk rana, lokacin da aka tambaye shi game da rahoton da ya bayyana cewar Amurkan na ma kasar leken asiri a kan kamfanin wayar nan ta Huawei, tsaffin shugabanninta, ma'aikatunta na gida da na kasashen waje har ma da bankunanta.
Mr Hong ya ce Sin ta damu kwarai game da rahotannin da ke nuna yaduwa, yana mai bayanin cewa kafofin yada labarai sun riga sun bayyana wassu bin kwakkwafi da binciken sirri da kuma satan bayanai da Amurka ke yi a kan wassu kasashe da suka hada da kasar Sin.
A don haka in ji kakakin ma'aikatan harkokin wajen ya ce Sin na bukatar Amurka ta yi bayani game da hakan, sannan kuma ta dakatar da irin wannan aikin. (Fatimah)