in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na shirin shiga zango na biyu na bunkasar tattalin arziki
2014-03-23 15:48:23 cri
Yanzu haka kasar Sin na daf da shiga zango na biyu na bunkasar tattalin arziki, bayan cimma nasara a zango na farko, matakin da ya sanya kasar samun managarcin ci gaba cikin gajeren lokaci.

Shugabar asusun ba da lamuni na IMF Christine Legarde ce ta bayyana hakan a yau Lahadi, yayin da take jawabi gaban mahalarta taron tattauna batutuwan ci gaba da ake gudana a nan birnin Beijing.

Legarde ta kara da cewa, sauyin da kasar ta Sin ke nufin aiwatarwa ya kunshi cimma tabbatattun manufofi dake bisa managarcin tsari, tare da la'akari da bukatun kasa da kasa.

Haka zalika shugabar asusun na IMF ta bayyana sabbin tsare-tsaren da kasar ta Sin ke nufin aiwatarwa, wadanda ke kunshe cikin kudurorin da aka cimma, yayin cikakken zama na 3 na kwamitin tsakiyar jam'iyyar kwamins karo na 18 a matsayin wani ginshikin cimma inganci, nagarta, da ci gaba mai dorewa a dukkanin fannonin bunkasa kasar.

Ta ce duk da kalubalen dake tattare da wannan aiki, ta yi imanin kasar ta Sin na da ikon samun tarin nasarori kamar yadda ta saba yi a baya. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China