in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci kasashen Africa dasu fito da wadan su manufofi da za su tallafawa matalauta
2014-03-21 11:26:52 cri
A ranar Alhamis ne, Majalisar Dinkin Duniya ta yi kira a kan gwamnatocin kasashen Africa da su fito da wadansu manufofi da za su tallafa wa matalauta domin a kawo karshen matsalar talauci.

Datrektan yankin Africa na kamfe din manufofin ci gaban wannann karni, Charles Abugre ya ce ana bukatar wani ginshikin matakai da zai kunshi kowa da kowa, domin ta haka ne kawai za a kai ga cimma inganta rayuwar matalauta dake nahiyar Africa.

A yayin da yake jawabi lokacin kaddamar da rahoton duniya a kan tsananin talauci, Mr. Abugre ya ce ya kamata Africa ta bullo da tsari na bai daya, wanda zai kawo canji ga rayuwar talakawa marasa galihu.

Rahoton ya ce yawan mutane dake fama da rashin ilmin zamani da kuma matsalar rauni na mulki na daga cikin abubuwan da suka haddasa yawan talauci na duniya.

Charles Abugre, ya shawarci Africa da ta mai da hankali wajen aiwatar da ci gaba a shekaru 15 masu zuwa.

Abugre ya kara da cewa a karon farko a cikin tarihi, shugabannin nahiyar ta Africa za su mai da hankali a kan ajanda guda, wacce ake sa ran za ta murkushe matsalar talauci.

Mr. Abugre ya ce cimma manufofi na kafa masana'antu gadan-gadan na daya daga cikin hanyoyin da za su dakushe talauci saboda kasancewar kafuwar masana'antu za ta haifar da guraban ayyukan yi ga jama'a.

Mr. Kwende Mwekdwa, mai kididdiga dake cibiyar bincike da kididdiga a kan manufofin gwamnati ta kasar Kenya ya bukaci Nahiyar Africa da ta aiwatar da canji a kan yadda suke tafiyar da tsare tsarensu ta yadda tatttalin arzikin nahiyar zai kaucewa dogara a kan kayayyakin da ake fitarwa zuwa kasashen ketare.

Kamar yadda ya ce, hakan zai kawo karuwar darajar ababen da ake samarwa a cikin kasashen, wannan kuma zai haifar da rayuwa mai dorewa a Africa. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China